ABIN KAUNATA RASULULLAHI(S.W.A)
-Muhammad Mahmud Yarima
1. Da sunan Jalla mai baiwa
Gwanin nan wanda yai kowa
2. Na ke son fara wakena
Da zan ma Mustafa nawa
3. Muhammadu dan Amina na
Imamul muttakiinawa
4. Salati hadda taslimi
Ga jinkan addananawa
5.Da alaye, sahabbai har
Da az’wajinsa kyawawa
6. Ina rokon Ka Ya ALLAH
Ka min Kyauta da ‘yar baiwa
7. Ta in zan yin yabon manzo
Da yin raddi ga arnawa
8. Ka ban ikon ta kai baiti
Dari cif babu yankewa
9. Ka ban dama ta in tsara
Ta hau tsaf babu karyewa
10. Ma- faa-ii-lun, Ma-faa-ii-lun
Ma’aunina ga tsarawa
11. A Fadin duniyar nan kaf
Gabas, yamma, arewawa
12. Zuwa yau dagga can farko
Bakar fata da lar’bawa
13. Ba ai da mai kamar kai ba
Cikin turarai da aj’mawa
14. A kyan hali da fuska ma
kawai kai ne ka burgewa
15. Ado nai gaskiya kullum
Kazib, bai kirkirantowa
16. Irin halin Aminullah
Ina mai ma Kwatantawa
17. Bale ma har a ce ya kai
Ga cimma Dan kuraishawa
18. Muhammad Sayyidul âlam
Uba gun duk talakkawa
19. A kyauta ba shi yin kwauro
A don tsoron talaucewa
20. Khalilullahi Dan lele
Na Allah mai azurtawa
21. A harka ba shi yin kwange
A zance ba ya hargowa
22. Liwa’ul hamdi sai dai kai
Maceci gun mu ran tsaiwa
23. Abin kauna Rasulullah
Abin bi babu tabewa
24. Kira na gunku al’umma
Ku tsinewa yahudawa
25. Da Ke zagin habibullah
Masoyin mai halittawa
26.Wabillah ! Kun kade arna
Mutan banza Amurkawa.
27. Mutan Den mark na fir’auna
Irin aikinku sai wawa
28. Da sauraran masu kin manzo
Diyan wofi faransawa
29. Masifu har bala’o’a
Ka jibga kan su daddaiwa
30. Ka dora kansu kaskancin
Da ba rana ta daukewa
31. Ku ce amin masallata
Ku amsa min da gaggawa
32.Ina arna la’an tattu
Da mushrikai, majusawa
33. Munafukkai da ‘yan tsafin
Bakar fata da turawa
34. Ku binne kanku don haushi
Muhammad ya wuce kowa
35. Mukami gun sa har ga kai
Munâjâti na ganawa
36. Da Jallallahu; can sammai
Ya keta babu kangewa
37. A arnan duniya kwata
Gaba dai ban cire daiwa
38. Mutane har da aljannu
Da mai ‘yanci da ma bawa
39. Arab ne ko bakar fata
Bamanagole da turkawa
40. Na farko har zuwa karshe
Suna tsoro Rasul nawa
41. Da zarar sun ji sunansa
Gaba dai dimaucewa
42. Bale ma har a ce yaki
Matsafa sai fa watsewa
43. Su ruga can cikin daji
Ya karnai basu waigowa
44. Muhammad jarumi gwarzo
A fama baya juyawa
45. Kwamanda ne a gun yaki
Tsayayye babu rugawa
46.A komai kai na ke son bi
Ina zan so musanyawa
47. Na’am, sunnarka dadin bi
Da sauki ba tsanantawa
48. Ina ma da ace na zo
A loton Dan Hishamawa
49. Makaucewar idanuna
Ya zan ya sami warkewa
50. Dalilin ban ga Manzo ba
Makaho ne ni, baubawa
51. Rashin in gan ka Ya Manzo
Ya kan sa in ta kokawa
52. Uhm! Ni dai takaicina
Rashin yakar badardawa
53. Da ban sa’ar zuwa nai ba
A ban lambar shahidawa
54. Mahaifina a gaisheka
Ina kauna da godewa
55. Da sunan nan da kas sa min
Irin sunansa kyakkyawa
56. Ina kaunar Ka Ya Manzo
Da fatan in zamantowa
57. Cikin gaiyar masoyanka
A can ranar lisaftawa
58. Ina shauki da begenka
Khalilin mai hukuntawa
59. Dado yardarKa Ya Allah
A kan az’waj da ah'lawa
60. Su Hafsat, A’isha, Saudat
Da Ramlat ba ni mantawa
61. Da Zainab Bintu Jah’shin har
Da Zainab ‘yar Khuzaimawa
62. Juwairiyya, Safiyya har
Khadijat, Ummu Salmawa
63. Da Maimunat diyar Haris
Cikon sha dai a kirgawa
64. Uwaye ne a gun kowa
Da kowa banda gaulawa
65. Bakin arne da mai zagin
Su; zindiki, kare gawa
66. Ga ‘ya’ya nai na kirkin nan
A yanzun zan lisaftowa
67. Batula: Fâtima Zahra
Da ‘ya’yan gunta Husnawa
68. Su Kasim, Ummul Khulsumin,
Mu’azzam dan kusaiyawa
69. Rukaiya har da Abdullah
Da Zainab ‘ya ta nunawa
70. Iyalai ne gidan Manzo
Na Allah ba musantawa
71. Ina kaunarku ba shakka
Gaba dai babu warewa
72. Zunubbaina na ke hange
Da wautata da sabawa
73. Tunanin kar su kakkange
Ni; kaiwa gun ka dan baiwa
74. A ranar nan da bayi duk
Kiyaman ba tsugunnawa
75. Ina rokon Ka Ya Allah
Ka ban dama ta ganawa
76. Da manzo mai ruwan tafki
Na kausar ba musantawa
77. Ina biro da harshena
Ku zo nan mui ta tsinewa
78. Yahudawa da ‘yan iska
Mutan turai, nasarawa
79. Haba! Sun zagi Manzona
Ta ya ya za ni kyalewa
80. Ina barranta da nisanta
Da dukkannin kiristawa
81. Da arnan nan na can Den mak
Miyagun har faransawa
82. A tsammaninsu taronsu
Na dangi babu rushewa
83. A duk taron da za kui kaf
ku san karshenku watsewa
84. A harka baya gaggawa
A zance baya hargowa
85. Irin Manzonmu mata duk
Na yau sun kasa haihowa
86. Ina! Wane mutum?, ai har
Kiyama ba a samowa
87. Ba ai tamkarsa can da ba
Iri nai ba a karawa
88. Uwata har da babana
Su zan fansa ga Kyakkyawa
89. Muhammad mai dubun kyauta
Na Hafsat Dan Kilabawa
90. Hakika ni ba zan kai ba
Irin Hassaan a wakewa
91. Da yin raddi ga arna duk
Ina fatan misaltawa
92. Ina gaida ka ya Hassaan
Mawakin mai madinâwa
93. A gun Allah Ta’ala dai
Nake kakkara godewa
94. Da ikon nan da yab ba ni
Na yin raddi ga arnawa
95. Ta’ala Kai dadin tsira
Ga Mâhï Wanda bai rowa
96. Muhammad mai cikar kira
Na Ramlat Dan kinanawa
97. A nan ne zan tsaya; ta kai
Dari cif babu yankewa
98. Nakumbon Malama Asï
Abokin dan rikadawa
99. Akan ce mai Yarimah Dan:
Gidan Maude na Madâwâ
100. Ya tsaro wanga baitoci
A reras babu tsinkewa
Monday, September 28, 2009
Thursday, September 24, 2009
MY WIFE should be
MY WIFE
Should be
Friendly and calm not termagant
Benign and patient not lousy
Kind and humble not arrogant
Slender and pretty not clumsy
Mild and wise not illiterate
Esteem and cheerful not worthless
Good and content not always in debt
Healthy and caring not careless
Just and honest not eloper
Talking and whispering not in jargon
Chatting and teasing not in anger
Peaceful and happy not forlorn
Native lady not immigrant
Skilful and tidy not Slovene
Fine and graceful not recalcitrant
Dressy and demure not vixen
Should be
Friendly and calm not termagant
Benign and patient not lousy
Kind and humble not arrogant
Slender and pretty not clumsy
Mild and wise not illiterate
Esteem and cheerful not worthless
Good and content not always in debt
Healthy and caring not careless
Just and honest not eloper
Talking and whispering not in jargon
Chatting and teasing not in anger
Peaceful and happy not forlorn
Native lady not immigrant
Skilful and tidy not Slovene
Fine and graceful not recalcitrant
Dressy and demure not vixen
FURFURA
FURFURA
1.
Ya makagin duk halittu
Wanda ke baiwar sarautu
Yai musulmi har batattu
Yay yi mata masu shantu
Kai na fara anbatowa
2.
Kara tsira mai yawaita
Gun Rasul mai kyau da tsafta
Har da alayensa kwata
Sa sahabbai masu bauta
Masu kaunar kyautatawa
3.
Duk da cewa shekaruna
‘Yan kadan ne kankanana
Furfura ta sauka kaina
Gargadi in gyara kaina
Yanzu kar in zan sakewa
4.
Zamani na wuwwucewa
Mautu ma na zagayawa
Ga ni na dau furfurewa
Al’bishir ke nan ga cewa
Mautu ce ke mammatsowa
5.
Dan jikina ya yi laushi
Shekaru sun tankwara shi
Furfura ta canza gashi
Yai fari tamkar na leshi
Yanzu sai dai rirrinawa
6.
Dole in bar shantakewa
Babu zancen shakatawa
Jin kida har rausayawa
Balbu sauran gulmatawa
Sai ibada ba tsayawa
7.
Sai su azkar, nafiloli
Yin tahajjud, aiki jamili
Bin tafarki sak a fili
Banda aiki ba dalili
Kar na zan dan kirkirawa
8.
Sai lizimtar yin salati
Kauracewa shirya “Party”
Banda bin mata a titi
Kar na koma jin su sauti
Furfura na tsawatarwa
9.
Da tunanina da homa
Bai wuce mata da gulma
Na haye doki na zulma
Na ki hankalta na koma
Sai kwatsam ga furfurewa
10.
Malaman kirki na sunna
Sun fada kar mui ta barna
Kar mu koma mui ta sauna
Kar mu shashance mu zauna
Lokaci na kukkurewa
11.
Nai biris na kama Danni
Kurciya na zizziga ni
Babu aune sai fa ga ni
Yanzu don Allah ku ji ni
Furfura ta mamayewa
12.
Na nutse neman bareyi
Na yi sabo masu nauyi
Ga shi gabbai sun yi sanyi
Taimakan Allah ga sauyi
In bi hanyar kyautatawa
13.
Jallah Kai ne Al’gafuru
Kar ka sa in zan mariru
Masu yin tubar muzuru
Ko ko tsufan “John”a zuru
Ma su sabo ba kulawa
14.
Rabbi kai n eke da jannah
Taimakan aiki na jannah
‘Yar wazifa kar na daina
Hadda wurdin nan na sunnah
Har zuwa na can kushewa
15.
Rabbi bawan nan Nakumba
Dan gidan Zainab da Abba
Ke bidar af’warKa babba
Babu shakka ya fa duba
Nesa ce ke kukkusowa
16.
Zan tsaya nan don na huta
Wag ga waka wadda nai ta
Baituka sha shidda kwata;
Gargadi don zuciyata
Kar ta ja min babbakewa
1.
Ya makagin duk halittu
Wanda ke baiwar sarautu
Yai musulmi har batattu
Yay yi mata masu shantu
Kai na fara anbatowa
2.
Kara tsira mai yawaita
Gun Rasul mai kyau da tsafta
Har da alayensa kwata
Sa sahabbai masu bauta
Masu kaunar kyautatawa
3.
Duk da cewa shekaruna
‘Yan kadan ne kankanana
Furfura ta sauka kaina
Gargadi in gyara kaina
Yanzu kar in zan sakewa
4.
Zamani na wuwwucewa
Mautu ma na zagayawa
Ga ni na dau furfurewa
Al’bishir ke nan ga cewa
Mautu ce ke mammatsowa
5.
Dan jikina ya yi laushi
Shekaru sun tankwara shi
Furfura ta canza gashi
Yai fari tamkar na leshi
Yanzu sai dai rirrinawa
6.
Dole in bar shantakewa
Babu zancen shakatawa
Jin kida har rausayawa
Balbu sauran gulmatawa
Sai ibada ba tsayawa
7.
Sai su azkar, nafiloli
Yin tahajjud, aiki jamili
Bin tafarki sak a fili
Banda aiki ba dalili
Kar na zan dan kirkirawa
8.
Sai lizimtar yin salati
Kauracewa shirya “Party”
Banda bin mata a titi
Kar na koma jin su sauti
Furfura na tsawatarwa
9.
Da tunanina da homa
Bai wuce mata da gulma
Na haye doki na zulma
Na ki hankalta na koma
Sai kwatsam ga furfurewa
10.
Malaman kirki na sunna
Sun fada kar mui ta barna
Kar mu koma mui ta sauna
Kar mu shashance mu zauna
Lokaci na kukkurewa
11.
Nai biris na kama Danni
Kurciya na zizziga ni
Babu aune sai fa ga ni
Yanzu don Allah ku ji ni
Furfura ta mamayewa
12.
Na nutse neman bareyi
Na yi sabo masu nauyi
Ga shi gabbai sun yi sanyi
Taimakan Allah ga sauyi
In bi hanyar kyautatawa
13.
Jallah Kai ne Al’gafuru
Kar ka sa in zan mariru
Masu yin tubar muzuru
Ko ko tsufan “John”a zuru
Ma su sabo ba kulawa
14.
Rabbi kai n eke da jannah
Taimakan aiki na jannah
‘Yar wazifa kar na daina
Hadda wurdin nan na sunnah
Har zuwa na can kushewa
15.
Rabbi bawan nan Nakumba
Dan gidan Zainab da Abba
Ke bidar af’warKa babba
Babu shakka ya fa duba
Nesa ce ke kukkusowa
16.
Zan tsaya nan don na huta
Wag ga waka wadda nai ta
Baituka sha shidda kwata;
Gargadi don zuciyata
Kar ta ja min babbakewa
Subscribe to:
Posts (Atom)