Tuesday, July 12, 2016

QUR'AN AND MATHEMATICS

Muhammad Mahmud Yarima Nakumbo
Ramadan 1423/November 2002



QUR’AN AND MATHEMATICS



IN THE NAME OF ALLAH THE BENEFICENT THE MERCIFUL



God Almighty said, “We have not left anything out of the book (Alquran)”


“………. Ask the follower of the remembrance (learned), if you know not.” (Nah1: 43)



1. ADDITION I
God said,…….. “And whosoever cannot find (Such gifts) then a fast of three days while on the pilgrimage, and of seven when ye have return, that is ten in all…” [Baqara:196].


ANALYSIS:
Three days while on pilgrimage and of seven when ye return that is ten in all
3 + 7 = 10




2 ADDITION II
God Almighty said, “LO ! those of old and those of later time , will be brought together…………. (Waqia :49-50)
ANALYSIS
This simply means old account and recent account added together = Total sum of what one has recently




3. ARITHMETIC PROGRESSION
God said, “we created man from a product of wet earth, then placed him as a drop of seed in a save lodging, then fashioned We the drop a clot then, fashioned We the clot a little lump, then fashioned We the little lump bones, then clothed the bones with flesh and then produce it as another creation…” (Muminun: 12-14)


ANALYSIS
Prophet (P.B.U.H) said, “The parts that make man are collected for forty days as a drop of seed, then become a clot of thick blood for forty more days, Then the parts become a lump of flesh for forty days…….


THE VERSE STATED THAT PROPHET
SAID
- Man was placed as a drop of seed 40 days
- The drop is then fashioned into a clot 80 days
- The clot is then fashioned into a lump 120 days
- The lump is then fashioned into bone 160 days
40, 80, 120, 160. A.P
Common difference Between Successions = d = 2nd – 1st = 3rd – 2nd = 4th – 3rd
= 80 – 40 – 80 = 160 – 120
= 40 days
First number of days = a = 40 days
L = number of at nth succession
L = a + (n-1) d
At the 3rd succession, n = 3
L = 40 + (3-1) (40) = 120 days = For making a living fetus in a Mother’s womb.



4. ASCENDING ORDER
God said, “He it is who created you from dust, then from a drop (of seed then from a clot, then bringeth you forth as a child, then (ordained) that ye attain full strength and afterward that ye become old men….. [Ghafir: 67]


ANALYSIS.
Drop of a seed
Clot
Child hood
Full Strength
Old hood
40 days
80 days
270 days
480 months (40 yeas)
840 months
1 month, 10 days
2 months 20 days
9 months
As it was stated in Ahqaf :15
70 years
Thus, 1 month 10 days, 2 months 20 days, 9 months, 480 months, 840 months.

5. CALENDAR
God said, “Lo! The number of the months with Allah is twelve months by Allah’s ordinance in the day He created the heavens and the earth. Four of them are sacred… (Tauba: 36)

ANALYSIS:
Twelve months make a year.
Number of days we have in a leaf year = 366 days
This verse comes in the 9th chapter of the glorious Qur'an and it is the 36th verse in the chapter.
36 x 9 = 324
The verse stated, “… In the day that He (Allah) created heavens and the earth.” And God created the heaven and the earth in six days as it was stated in Chapter 7:54. The number of days we have in a week is seven.
6 x 7 = 42. Then 324 + 42 = the number of days we have in a leap year (366)


6. MULTIPLICATION
God said, “the likeness of those who spend their wealth in Allah’s way is as the likeness of a grain which growth seven ears, in every ear a hundred grain ….. “ [ Baqara:261]


ANALYSIS
To know the number of grains all together = seven multiplied by hundred grains = seven hundred




7. NETS
God said, “…. For thus Assamiri proposed. Then he produced for them a calf of a body ……. [Taha:87 – 88].


ANALYSIS
The final product of nets is model. For instance, to net a pyramid with square base would be:


THE VERSE STATED THIS MEANS
- Assamiri proposed = He made a nets
- Then produced a calf
of a body = He produce a model of calf

8. SETS
God said, “Then we gave the scripture as inheritance into those whom we elected of our bond men. But of them are some who wrong themselves and of them are some who are lukewarm, and of them are some who outstrip (others) through good by Allah’s leave that is the great favour!
Garden of Eden! They enter… And they say praise be to Allah who hath put grief away from us…’
[Fatir: 32-34]
ANALYSIS
Those who will enter paradise are of three categories
C = {some who wrong themselves; have no grief}
B = {some who are lukewarm: have no grief}
A= {some who outstrip others: have no grief}
Venn diagram
see foot note (Figure 1)
see foot note (Figure 2)



9. SPEED
God said, “And unto Solomon (We gave) the wind whereof the morning course was a month’s journey and the evening course a month’s journey…. “
(Saba: 12).
ANALYSIS
Speed = Distance/Time
Time = Morning course is from 12 midnight to 12 mid day which is equals to 12 hours.
Therefore morning course + evening course = 24 hours.
Distance = A vehicle that goes 56km per hour can cover a distance of 1,344km per day.
Morning course = 1 month’s journey
Evening course = 1 month’s journey
2 months = 60 days x 1,344km ]
= 80,640 km
SPEED = 80,640 km/24 hours
= 3360 km/h


10. SUBTRACTION
God said, “And verily we sent Noah into his folk, and he continued with them for a thousand year save fifty years…… “ (Ankabut: 14).

ANALYSIS
A thousand year save fifty years
1000 __ 50 = 950
END
Alhamdu lillahi

Friday, January 2, 2015

ZANCEN GASKIYA



Zancen Gaskiya
﴿ظهرالسد فى البر والبحر بما كسبت أيدى الناس ليذيقهم بعض الذى عملوا﴾
A lokacin da zan rubuta wannan takarda, babu shakka alqalamina da idanuwana na  kukan baqin cikin yadda a yau musulmai suka tsinci kansu musamman a Najeriya da kuma duniya baki xaya.
Na san cewa wannan takardar za ta sha tsokaci, gyara, qarin bayani, sharhi har ma da raddi. Ina roqon ‘yan uwana ma su yin raddi da su yi raddinsu a bisa adalci da tsoron Allah.
Mun ximauce muna neman mafita daga halin da muka tsinci kanmu a yau. Amma duk wanda ka zauna kana hira da shi sai ka ji yana cewa ai shekarar 2015 ba za mu yarda ba sai mun kayar da Mai-Nasara na yankin inyamirai. Tunaninmu gaba xaya ya taqaitu ga samun shugaban da za’a daina kashe mu, mu samu kudi da kwanciyar hankali. Ba ma tunanin ya ya zamu dawo da martabar addinin Musulunci a qasar; mu dai a daina kashe mu, mu ci gaba da kasuwancinmu da tara dukiya da mata.
Ina rantsuwa da sunan Allah, duk wani uzuri da za mu yi ta ba kanmu, da duk wata hila da kwana-kwana ba za su fitar da mu ba sai mun koma ga addinin Allah, ya zama Shari’ar Allah ita ke motsi a qasar. Allah Ya sa a fahimce ni a bayanai na da za su zo a gaba.
Bari mu kalli qasar gaba xaya ta fuskar:
 a) Shugabanci
Haqiqa duk mai hankali ya san cewa babu wani tsarin mulki babba da ake bi a duniya na dimokaraxiya ko mulkin soja wanda ba’a yi ba a wannan qasar tamu Najeriya, amma babu wani sakamako mai kyau da suka haifar in ba kashe shugabanin kirki ba, ruguza qasa da son maida ita kan wani tafarkin da bai dace da mu ba. Tsarin mulki xaya ya rage wanda ba’a yi ba a Najeriya, kuma ina rantsuwa da sunan Allah shine tsarin mulkin da zai kawo dukkan jin daxi da adalci da zaman lafiya mai xorewa a wannan qasar. Wannan tsarin shine Mulkin shari’ar musulunci. Sai dai abin tambaya a nan shine shin da irin wannan demokaraxiyar za’a samar da mulkin musulunci a Najeriya??!!
Wallahi a tarihin duniya ba’a tava yin haka ba. Ai ya ishe mu kyakkyawan misali abinda ya faru a qasar Misra (Egypt). Idan can Egypt ya yi mana nisa, to mu tambayi kanmu da kanmu: Ina makomar shari’ar Zamfara da sauran jihohin arewa?!
A kullum kira ake ta yi cewa a je ayi rajista, a jefa quri’a, mu zavi mutanen kirki masu kishin qasa, ba don komi ba sai don a samu zaman lafiya, walwala da qaruwar arziki. Wani lokaci har mu kan ce “Ai in ba zaman lafiya a qasa ko addinin ma ba za’a yi yadda ya dace ba.” A dai-dai lokacin mun manta da faxin Allah cewa:
﴿... وَالْفِتْنَةُ أَشَدُّمِنَ الْقَتْلِ
ma’ana: “Yin kafirci (a bayan qasa) shi ya fi yaqi tsanani”
Ai dai ga shi nan! Kullum siyasar muke yi, zaven mu ke yi, amma kullum cikin wahala mu ke qara shiga. Daga qarshe, kowa ya ga inda demokaraxiya ta kai mu a yau.  Abin mamaki, waxanda mu ka zava sune jagororin qasar, amma kuma ga musibu sun baibayemu. Anya! Ba wani abu kuwa??!! Anya! Ba’a kauce hanyar ba??!! Idan mun ce ma za mu yi demokaraxiyar a bisa lalura, to me ya sa ba za mu xauki shawarar da babban malami Muhammad Auwal Adam Albani ya ba musulmin Najeriya ba? [1]
A wajen duk wani musulmi mai kwana da tunanin addinin musulunci a ransa ya san cewa hanya xaya ce za ta kai mu ga tabbatar da addininmu a wannan qasar, sai dai a   kullum gudunta mu ke yi, muna cewa wai ba mu da qarfi, lokaci bai yi ba, sai dai kurin cewa ai muna da yawa a qasar. Hanyar kawai ita ce JIHADI. Wai! Tabxijan! a nan na san da yawan musulmai za su ce: kun ji wani mahaukaci, me muke da shi da za mu yi jihadi? Ina rantsuwa da sunan Allah, wannan xabi’ar ta sa muka manta da cewa jihadi wanzajje ne har zuwa tashin qiyama. Na cika da mamaki, ranar 17/8/2014 mu na karatu a makarantar islamiyya babin janaza. Da aka yi maganar yadda ake rufe shahidai, sai wata mata ta ce “wannan karatun mutanen da ne don yanzu ba jihadi.[2] Ka ga har an manta da cewa Annabi  (s) ya ce:
مَنْ مَاتَ وَلـَمْ يَغْزُ وَلـَمْ يـُحَدِّثْ نَفْسَهُ بِهِ مَاتَ عَلَى شُعْبَةٍ مِنْ نِفَاقٍ. رواه مسلم
Ma’ana:
Wanda duk ya mutu bai yi jihadi ba, kuma
bai  ma sa a ransa  cewa zai yi jihadi ba, to,
ya  mutu  a  wani  bangare  na   munafunci.
  
Jama’a da gaske na ke yi ina nufin jihadi na gaskiya, ba “jihad week” ba wanda ake barinsa a “campus” in an gama makarantar, ba jihadin baki ba. waxannan suna daga cikin abubuwan da suka jawo mana halin da muke ciki. Eh mana! Mun yi ta kurarin jihadi da baki kawai a qasar nan, wanda hakan ya tsorata wasu mutane a qasar, su ka shiga tara makamai, daga qarshe da suka gano abin duk bula ne, sai suka afka mana da kisa da walaqanci a wasu garuruwan arewacin Najeriya.
Allah Ka nuna mana ranar da za mu samu shugaba tsayayye wanda duk mutanen Najeirya za su yi masa mubaya’a ta yadda in ya yi umurni da mu fito, shi ke nan an gama. Allah Ka amsa mana. Amin!
A yau gaba xaya mutanen Najeriya sun makauce suna neman canjin gwamnati. Amma ba gwamnatin addini ba; su dai kawai a samu jin daxi da walwala. A maimakon musulmi su yi tunanin ya ya za’a ce musulunci ya mulki Najeriya, sai suma kawai suka koma suka kama tafarkin kafirar siyasar Najeriya, kai da qafa.
Mu tuna in mun manta cewa tunda Najeriya ta samu ‘yancin kai har zuwa yau, kafirci ke mulkin Najeriya kuma shi ke jan ragamarsa yadda ya so a qasar. Me yasa na ce haka? Ta yiwu wani ya ce ia musulmi sun sha yin shugabanci a Najeriya. Tabbas haka ne, amma ai ba da shari’ar Allah suka yi shugabancin ba. Kuma ba a lokacin mulkin xaya daga cikin musulman ba ne aka so a sa qasar cikin qungiyar qasashen musulmi na duniya ba? Amma da qungiyar arnan Najeriya ta ce ba ta yarda ba, haka nan aka kashe maganar har hazal yaum.  Dubi yadda arnan arewa suka afka ma musulmi a garuruwan Jos da Yalwan Shandam …. a nan arewacin Najeriya, suka kashe mutanenmu, suka qona dukiyoyinmu, suka kwashe matayenmu waxanda har yau suna can a hannunsu amma ba abinda aka yi. Gwamnati ba ta yi komai ba, mu kuma son duniya da tsoron mutuwa sun hana mu yin wani abu; kamar yadda Annabi (saw) ya faxa. Dubi irin kisar da suka yi ma musulmi a ranar sallah. Wai ina ‘yanuwantakar musulunci da ke tsakaninmu, wanda abin nan ya afku, ba xaya ba ba biyu ba, amma ba wani xauki da musulman qasar nan suka kai. Sai da aka gama abinda aka yi mu ka tara tsummokara da garin rogo mu kai musu. Abinda muka iya ke nan.  A yau kuwa Mai-Nasara na yankin inyamirai da qungiyar arnan Najeriya sun haxa kai sai sun ga bayanmu. Ba su son su ga muna addininmu. A nan na ke son ‘yan-uwa musulmi su san cewa samu daular duniya a qarqashin rashin bin dokar Allah, wahala ne kawai. Allah Ya kai haske qabarin Alfazazi da ya ce:
إِﺫَاالدِّينُ لَمْ يَكْمُلْ فَلاَ كَانَتِ الدُّنْيَا
Idan har ba za’a yi addinin (Allah) ba (a bayan qasa) to, babu amfanin wanzuwar duniya (gwamma duniyar ta tashi)    
Ya ku ‘yan uwana musulmin Najeriya, muna tunanin a yau idan aka buga kugen siyasa, muka zavi xan arewa musulmi, shi ke nan arnan nan za su bar mu a irin qarfi da xaurin gindin da suke da shi a qasar da sauran qasahen duniya masu goyon bayan ta’addanci?! Qarfinsu a yau ya kai ga su yi odar makamai jirgi guda wanda gwamnatin tarayya ce kawai zata iya sayen irinsu, kuma huxxar cinikinsu ma sai qasa da qasa.
Sai dai qungiyar CAN ba ta yi laifi ba. Eh, mana! Mu fa Allah Ya gaya mana a cikin qur’aninmu cewa:
﴿ وَأَعِدُّوا لـَهُم مَّاسْتَطَعْتُم مِّن قُوَّةٍ وَ مِن رِبَاطِ الـْخَيْلِ تُرْهِبُونَ بِهِ عَدُوَّ اللهِ وَعَدُوَّكُمْ
Ma’ana: Ku yi musu tattali na qarfi (makaman harbi) da turkakun dawakai don razanar da maqiyan Allah kuma maqiyanku

Amma abin mamaki gaba xaya musulman Najeriya mun yi shakulatin vangaro da wannan umurnin na Allah.
Su kuwa da Bible ya ce musu a cikin Luke 22: 36 “ …And he who has no sword, let him sell his garment and buy one.” Ma’ana: “…. Duk wanda ba shi da makami to, ya sayar da suturarsa ya sayi (makami).”  Sai ga shi har odar jirgin makamai su ke yi.  Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un

b) Zamantakewa da rayuwa
A sanadiyar rashin gwamnatin musulunci mai adalci, a yau mutanen Najeriya na rayuwa ne yadda suka ga dama. Har ta kai ga cewa idan mutumin kirki ya aikata wani aikin da addinin musulunci ya yi umurni da  shi, sai ka ji ana cewa ai su malam wane akwai takura ma kai. Dubi yadda zina, shan giya, luwaxi, maxigo su ka bayyana a qasar nan. Cin haramun da riba kuwa waxannan ‘yan gida ne. Abin takaici shine yadda matan aure suka nutsa cikin harkar zina. Aiki ba da ilimi ba kuwa ya zama ado a gunmu. Zumunta sai wane da wane. Son juna kuwa a baki ne kawai. ‘Yan uwantakar musulunci sai kaxan. Kar ma mutum ya yi maganar haxin kai don babu. Taimakon addini a wajenmu shine kawai mu gina masallatai, Don haka a yau muka cika anguwanninmu da garuruwanmu da masallatai waxanda kawai muke cika su jikinmu. Kamar  dai yadda Annabi (saw) ya ce: “……sun cika masallatansu da jikinsu amma zuciyarsu ta rushe daga shiriya.”  Dukkan waxannan halayen, rashin tsayayyar gwamnatin musulunci ya sa suka zama ruwan dare a qasarmu. Mafi munin al’amarin shine ba mu da wani jagora ma takamaimai mai faxa aji.
Ya ku musulman Najeriya babu shakka an fa ci mu da yaqi, duk wani abu da za’a yi mana a yau mai-mai ne. Jama’a an fa tsere mana, duk  wani sauri ko gudu da za mu yi don mu cimma waxancan, tafiyar guragu ce kawai.[3]   
TO YANZU INA MAFITA?
Mafitar ita ce
1) Fadin Allah Maxaukaki da yake cewa
﴿وَعَدَ اللهُ الَّذِينَ ءَامَنُوا مِنْكُم وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ لَيَسْتَخْلِفَنَّهُمْ فِى الْأَرْضِ كَمَا اسْتَخْلَفَ الَّذِينَ مِن قَبْلِكُمْ وَلَيُمَكِّنَنَّ لَهُم دِينَهُمُ الَّذِى ارْتَضَى لَهُمْ وَلَيُبَدِّلَنَّهُمْ مِنْ بَعْدِ خَوْفِهِمْ أَمْنًا يَعْبُدُونَنِى وَلَا يُشْرِكُونَ بِى شَيْئًا وَمَنْ كَفَرَ بَعْدَ ذَالِكَ فَأُولَـــئِكَ هُمُ الْفَاسِقُونَ۝ ﴾ سورة النور : ٥٥                                               
Ma’ana:                      
Allah Ya yi alqawari ga waxanda suka yi imani suka aikata aiki na qwarai cewa Zai sanya su, su zama mamaya a cikin qasa, kamar yadda Ya sanya waxanda suka zo kafin ku; kuma (Allah) Zai tabbatar musu da addinsu wanda Ya yardar musu a gare su; kuma Allah Zai canza musu bayan tsoron da suke ciki zuwa zaman lafiya, su bauta mini batare da suna haxa ni da kowa ba. Duk waxanda suka kafirce bayan wannan to, waxannan sune fasiqai.
    
Bari mu dubi  ayar nan da kyau
i.) Allah Ya yi alqawari ga waxanda suka yi imani suka aikata aiki na qwarai …..
babu shakka imani na gaskiya shine matakin farko na cin nasarar duniya da lahira. Aiki na kwarai kuwa Annabi (saw) ya yi bayaninsa a lokacin da aka tambaye shi wane aikin alheri ne ya fi kowanne? Sai ya ce: JIHADI DON XAUKAKA KALMAR ALLAH. (Muslim)
ii.) (Allah) Zai tabbatar mana da addinmu wanda Ya yardar mana a gare mu; kuma Zai canza mana tsoron da muke ciki zuwa zaman lafiya.
Alqawarin Allah da Ya yi mana a wannan ayar Ya yi ne bisa sharaxin in mun yi imani kuma mun yi aiki na qwarai.
Ashe ke nan matakin farko shine mu kyautata imaninmu, mu so juna so na haqiqa  wanda babu khiyana a ciki. Daga nan sai mu roqi Allah Ya ba mu jagora tsayayye wanda duk wani musulmi zai yi masa mubaya’a. wannnan shine ginshiqin da muka rasa don haka muka kasance cikin ruxu da hayaniya, kowa na abinda ya ke so.

2) Faxin Annabi (saw) da ya ce:
“Idan dai ku ka koma (ba abinda ku ka sani kuma ba abinda ku ke yi) sai noma da kiwo, ku ka bar jihadi; Allah Zai xora muku wani irin walaqancin da ba Zai cire muku shi ba har sai kun koma  zuwa ga  addininku (da gaske kamar yadda ya ke.)” Wannnan kuwa ba mai musun cewa haka muka koma a yau. Maza da mata yaro da babba ba abinda muka tasa a gaba sai neman duniya. Inna lillahi wa inna ilaihi raji’una! A yau akwai matayen da ke kashe auren su don su koma makaranta, wai in sun gama su samu aiki a dama da su.

Allah Ka ba mu zaman lafiya mai xorewa. Ka qare mu da lafiyar da za ta zamo mana qarfi wajen rusa kafirci da zalunci a wannan qasar tamu mai albarka.


[1] Ban son in bayyana shawarar a nan soboda magabta
[2] Akan wannan maganar ne mu ka fitar da maqala mai suna jihadi na nan har tashin qiyama
[3] A wannan maganar na yi dungu a cikinta don bayyanata a zahiri zai sa magabta su ……………………………………

ME YA KAWO HAKA?



ME YA KAWO HAKA??!!
Na dade ina ta tambayar kaina wasu tambayoyi a zuci, har sai da ya kai ga cewa zancen zucina ya fito fili. Amma har yanzu da alkalamina ke rubuta wannan zancen zucin nawa, ban gano amsar da zan ba kaina ba.
Ku taimake ni don mu gano amsar tare.

Tambayar farko:
A zamanin da, malaman addini kan yi amfani da minti biyar kacal, wajen yin wa’azi ga mutane, wa’azin ya ratsa jikinsu, ka ga mutane na kuka suna qauracewa savon Allah ta sanadiyyar wannan wa’azin. Amma me ya sa a yau nake kwashe awa biyar ina wa’azi mai cike da balaga da hikima da qwarewa ta ilimi, amma wa’azin bai ratsa zuciyar mutane balle su bar abinda suke yi na savon Allah???!!! Ka ga idanuwanmu qarmadagau???!!!  

Tambaya ta biyu:
A da, kakata ta haqura ta zauna a gidan mijinta cikin wadatar zuci, ta gamsu da duk abinda kakana zai kawo mata. Amma me ya sa matata a yau ta lashi takobin sai ta fita ta yi aiki, da sunan wai ba komi zan iya yi mata ba, alhali ba na gaza ba ne???!!!

Tambaya ta uku:
Magabatanmu mutane ne masu mutunci da izza. Su ke faxa aji, su ke gitta kara ba’a tsallaka musu, sune iyayen gidan wasu, ba’a yi musu kallon raini. To me ya sa a yau raini da wulakanci ya baibaye mu, ya lulluve mu???!!! A cikin masu raina mun ma har da bayin kakanninmu!!!

Tambaya ta huxu:
A da za ka ga duk inda musulmi ya gamu da xanuwansa musulmi yana xaukarsa tamkar xan gidansu ne uwa xaya uba xaya. Ina irin wannan ‘yanuwantakar ina take a yau???!!!

Tambaya ta biyar:
A da Malamai da almajirai kowa na fafutukar neman lahira ne kawai, ba su siyar da addininsu don samun abin duniya qasqantacce, amma me ya sa a yau ni da malamaina ba mu da aikin yi sai ci da addini???!!!

Tambaya ta shida:
A da idan Musulmi xaya ya shiga wata damuwa gaba xaya za ka ga ‘yanuwansa musulmai sun shiga wannan damuwar; idan kuwa ya faxa hannun arna ne to ko za su qare sai sun je sun ceto wannan xanuwa musulmin. Amma me ya sa a yau mu ke komawa gefe idan wani ko wasu ‘yanuwa suka faxa cikin musiba???!!! Sai abin ya wuce mu kai mu su tsummokara da garin rogo!!!

Wallahi ba wani abu da zai gyara mu in ba abin da ya gyara mutanen farko ba.
Ba wata hanya da za mu bi martabarmu ta dawo in ba mun koma mun kama koyarwar addininmu ba sau da qafa.



Monday, August 5, 2013

ABIN KAUNATA LITTAFIN ALLAH: ALKUR'ANI

ABIN KAUNATA LITTAFIN ALLAH
A duk lokacin da tarihi ya maimaita kansa, ana son mutane su koma su dubi tarihin don su samo hanyar gyara, in abin ya shafi gyara ne. idan kuwa ya shafi karfafawa ne, sai a yi hakan.
A shekara ta goma sha biyu bayan hijira aka samu afkuwar yakin yamama, wanda a cikinsa ne aka kashe mahaddatan Alkur’ani daga cikin sahabbai masu dimbin yawa. A yau duk mai hankali ya shaida irin kisar mahaddata Alkur’ani da aka yi a Maiduguri. Babu shakka Allah kadai Ya san adadin mahaddata da makarantan Alkur’ani da aka kashe. Ba su ji ba, ba su gani ba, ba ci ba, ba su sha ba.
Bayan yakin yamama, sahabbai sun yi kokari wajen ganin cewa Alkur’ani bai salwanta bat a hanyar kasha mahaddatansa, suka yi aiki tukuru wajen tattarawa da rubuta alkur’ani a waje daya, wanda gajiyarsa ne muke ci a yau.
To mu kuma me za mu yi wa Alkur’ani ganin yadda aka rasa dimbin mahaddatansa a waki’ar da ta faru?
KOKARIN DA ZA MU YI SHINE, DON ALLAH, KOWANE GIDA NA MUSULMI DA KE WANNAN KASAR A TABBATAR DA CEWA AN SAMAR DA MAHADDATAN KUR’ANI A KALLA GUDA UKU. SANNAN YA ZAMA DUK MUTANEN GIDAN MAKARANTAN KUR’ANI NE.
Wannan shi ne kadai abinda za mu yi don ganin wanzuwar Kur’ani, kuma shi ne diyyar ko tukuicin da za mu biya wadanda aka kasha da shi.

HANYAR KYAUTATA DANGANTAKAR MU DA ALKUR’ANI
Shin ko muna cikin irin mutanen nan da ke karanta Kur’ani jefi-jefi, ko kuma ma ba ma karanta shi? Idan haka ne, ba ma tsoron ranar da Manzon Allah (saw) zai kai karar mu a gaban Allah (swa), ya nuna ma Allah mu, yana mai cewa Ya Ubangiji, wadannan sune suka kaurace ma Alkur’ani (a duniya).
Wadannan wasu hanyoyi ne da za mu bi wajen ganin mun gyara dangantakar mu da Alkur’ani.
1.     Mu tabbatar da mun je mun koyi karatunsa a gaban malamai kwararru masana karatunsa da fassararsa.

2.     Niyyar mu ta karatun Alku’ani ta zama don Allah ne kawai, ba don neman shahara ba. Sannnan mu tabbatar da cewa duk abinda muka karanta  mun yi aiki da shi gwargwadon iyawarmu.

3.     Idan ba ma iya daukar lokaci mai tsawo muna karanta shi, to mu fara da karanta shi na minti biyar a kowace rana. Da yardar Allah wannan minti biyar din zai koma minti talatin, har ya kai lokcin da za mu iya kwashe awoyi muna karanta shi.

4.      Mu tabbatar da muna sanin abinda muke karantawa. Ya kamata ace kowane gidan musulmi akwai Alkur’ani mai fassara da yaren da mutum ya ke ji.

5.     Kada mu takaitu ga karatunsa kawai, mu yi kokari mu dinga sauraren karatunsa a bakin wasunmu ko a kaset ko kuma a CD  

6.     Babban abu mafi muhimmanci shine addu’a. Mu yawaita rokon Allah Ya sa mu zama daga cikin masu karatun littafinSa dare da rana, Ya bamu ikon sanin ma’anarsa, Ya kuma azurata mu da yin aiki da abinda muke karantawa.

HANYAR GYARA KARATUN ALKUR’ANI
Babu wata hanyar da za mu gyara karatun Alku’ani in ba ta hanyar sanin tajwidi ba. Babban abu kuwa shine sanin mafitar haruffan larabci. Don in har za mu karanta kur’ani da lahajar mu ta Hausa to, babu shakka za mu dinga caccanza ma’anonin Kur’ani.
Misali, inda Allah Madaukakin Sarki ke cewa
1.     إنه عليم بذات الصدور
idan mutum ya karanta da hamza,  أليم  ya canza ma’anar daga Allah masani ne  ya koma Allah mai radadi ne. Subhanallah

  2. Haka nan inda Allah (swa) yake cewa مخلصين له الدين  idan mutum ya karanta da sinun  مخلسين ya canza ma’anar daga masu yi tsantsa saboda Allah zuwa masu yankan Aljihu. Subhanallah

3.     Haka nan inda Allah ke cewa وضل عنهم ما كانو يفترون   
Da mutum zai karanta da dalun      ودل shi ke nan mutum ya canza ma’anar daga  ya bace musu….  zuwa ya yi musu nuni ……

4.       Har ila yau da mutum zai karanta fadin Allah (swa)
 لا تخونوالله والرسول da kafun madadin kha’un ,   تكونو  لا ma’anar ta canza daga: kada ku ha’inci Allah da Manzon Allah zuwa kada ku zama Allah da Manzon Allah.
Da sauran irinsu.
Ashe ke nan dole ne mu koyi yadda ake furta kowane harafi na larabci don mu tsira daga irin wadannan kura-kuran

Aljazari na cewa:
“Dolen dole ne akan (makarantan Alkur’ani )
Ya zama abu na farko tun kafin su fara (karatun alkur’ani) su san
Mafitar haruffofa da siffofinsu ………
Wanda duk baya karanta kur’ani da tajawidi (ya zama) mai laifi
Domin da tajwidinsa aka saukar da shi, kuma a hakan ya kawo zuwa gare mu.”

بســـــــــــــم اللــــــــه الرحمــــــــان الرحيـــــــــــــم
اللهم رب السماوات السبع و رب العرش العظيم، ربنا ورب كل شىء فالق الحب والنوى منزل التـــــــــــــوراة والإنجيل و القرآن, أنت الأول فليس فبلك شـــــــــيء و أنت الآخر فليس بعدك شيء، و أنت الظاهر فليس فوقك شيء و أنت الباطن فليس دونك شيء
اللهم صل على محمد و على أهل بيته، وعلى أزواجه وذرياته، كما صليت على آل إبراهيم، إنك حميد مجيد، و بارك على محمد وعلى آل بيته، وعلى أزواجـــــــه و ذرياته، كماباركت على آل إبراهيم، إنك حميد مجيد
اللهم ربنا تقبل منا ختم القرآن و تجاوز عنا ما كـــان فى تلاوته من السهو والنسيان واكتبه منا على التمـام والكمال المهذب من كل الألحان. اللهم اجعل القــرآن لنا فى الدنيا قرينا، وفى القبر مؤنسا، وفى القيامـــــة شفيعا، وعلى الصراط نورا، و إلى الجنة رفيقا، ومن النار سترا و حجابا و الى الخيرات دليلا و إماما يـــا أكرم اللأكرمين. اللهم علمنا منه ما جهلنا وذكرنا منه ما نسينا واروقنا تلاوته وحفظه تأويله آناء الليــــــــل وأطراف النهار على الوجه الذى يرضيك عنا يا رب العالمين. اللهم اجعلنا من الذين إذا تليت عليهم ءاياتك زادتهم إيمانا. اللهم اغفر لإخوانن الذين سبقونا بالإيمان, وخصوصاإخواننا حفظ القرآن الذين قتلوا فى ميدغرى ظلما
اللهم يا خير الراحمين ارحمنا، ويا خير الغافريـــــــن اغفر لنا، ويا خير الرازقين ارزقنا و يا خير الفاتحين افتح لنا أبواب رحمتك كلها و خير الناصريـــــــــــن انصرنا، ويا خير حافظ احفظنا بما تحفظ به عبــادك الصالحين
اللهم بدل عسرنا يسرا، وضيقناسعة, وفقرنا عنـــى, وضعفنا قوة, وخوفنا أمنا وسلاما واستقرارا لنـــــــا ولسائر المسلمين يا رب العالمين
اللهم إنا نسألك خشيتك فى الغيب و الشهادة و نسألك كلمة الحق فى الغضب والرضى،ونسألك القصد فى الفقر و الغنى، ونسألك نعيما لا ينفد و قرة عيـــن لا تنقطع, ونسألك الرضا بعد القضاء وبرد العيش بعد الموت ومرافقة نبيك محمد صلى الله عليه وآله وسلم
ولذة النظر إلى وجهك والشوق إلى لقائك فى غيــــر ضراء مضر ولا فتنة مضلة
اللهم إنا نسألك بأنا نشهد أن لا إله إلا أنت الأحــــــد الصمد الذى لم يلد و لم يولد ولم يكن له كفوا أحـــد, يــــا ذالجلال والإكرام يا حي يا قيوم أن تفتح لأدعيتنا أبواب الإجابة يا من إذا سأله المضطر أجابه يامــــــن فلق البحر لموسى يا فالق الحب والنوى يا حي يا قيوم يــــا ذالجلال والإكرام. ربنا آتنا فى الدنيا حسنة و فى الآخرة حسنة و قنا عذاب النار
اللهم صل على محمد و على أهل بيته، وعلى أزواجه وذرياته، كما صليت على آل إبراهيم، إنك حميد مجيد، و بارك على محمد وعلى آل بيته، وعلى أزواجـــــــه وذرياته، كماباركت على آل إبراهيم، إنك حميد مجيــد