ABIN KAUNATA
LITTAFIN ALLAH
A duk lokacin da tarihi ya maimaita kansa, ana son mutane su
koma su dubi tarihin don su samo hanyar gyara, in abin ya shafi gyara ne. idan
kuwa ya shafi karfafawa ne, sai a yi hakan.
A shekara ta goma sha biyu bayan hijira aka samu afkuwar
yakin yamama, wanda a cikinsa ne aka kashe mahaddatan Alkur’ani daga cikin
sahabbai masu dimbin yawa. A yau duk mai hankali ya shaida irin kisar mahaddata
Alkur’ani da aka yi a Maiduguri. Babu shakka Allah kadai Ya san adadin mahaddata
da makarantan Alkur’ani da aka kashe. Ba su ji ba, ba su gani ba, ba ci ba, ba
su sha ba.
Bayan yakin yamama, sahabbai sun yi kokari wajen ganin cewa
Alkur’ani bai salwanta bat a hanyar kasha mahaddatansa, suka yi aiki tukuru
wajen tattarawa da rubuta alkur’ani a waje daya, wanda gajiyarsa ne muke ci a
yau.
To mu kuma me za mu yi wa Alkur’ani ganin yadda aka rasa
dimbin mahaddatansa a waki’ar da ta faru?
KOKARIN DA
ZA MU YI SHINE, DON ALLAH, KOWANE GIDA NA MUSULMI DA KE WANNAN KASAR A TABBATAR
DA CEWA AN SAMAR DA MAHADDATAN KUR’ANI A KALLA GUDA UKU. SANNAN YA ZAMA DUK
MUTANEN GIDAN MAKARANTAN KUR’ANI NE.
Wannan shi ne kadai abinda za mu yi don ganin wanzuwar
Kur’ani, kuma shi ne diyyar ko tukuicin da za mu biya wadanda aka kasha da shi.
HANYAR
KYAUTATA DANGANTAKAR MU DA ALKUR’ANI
Shin
ko muna cikin irin mutanen nan da ke karanta Kur’ani jefi-jefi, ko kuma ma ba
ma karanta shi? Idan haka ne, ba ma tsoron ranar da Manzon Allah (saw) zai kai
karar mu a gaban Allah (swa), ya nuna ma Allah mu, yana mai cewa Ya Ubangiji,
wadannan sune suka kaurace ma Alkur’ani (a duniya).
Wadannan
wasu hanyoyi ne da za mu bi wajen ganin mun gyara dangantakar mu da Alkur’ani.
1.
Mu tabbatar da mun je mun koyi karatunsa a gaban malamai kwararru
masana karatunsa da fassararsa.
2.
Niyyar mu ta karatun Alku’ani ta zama don Allah ne
kawai, ba don neman shahara ba. Sannnan mu tabbatar da cewa duk abinda muka
karanta mun yi aiki da shi gwargwadon
iyawarmu.
3.
Idan ba ma iya daukar lokaci mai tsawo muna karanta
shi, to mu fara
da karanta shi na minti biyar a kowace rana. Da yardar Allah wannan minti
biyar din zai koma minti talatin, har ya kai lokcin da za mu iya kwashe awoyi
muna karanta shi.
4.
Mu tabbatar da
muna sanin abinda muke karantawa. Ya kamata ace kowane gidan musulmi akwai
Alkur’ani mai fassara da yaren da mutum ya ke ji.
5.
Kada mu takaitu ga karatunsa kawai, mu yi kokari mu
dinga sauraren karatunsa a bakin wasunmu ko a kaset ko kuma a CD
6.
Babban abu mafi muhimmanci shine addu’a. Mu yawaita
rokon Allah Ya sa mu zama daga cikin masu karatun littafinSa dare da rana, Ya
bamu ikon sanin ma’anarsa, Ya kuma azurata mu da yin aiki da abinda muke
karantawa.
HANYAR GYARA KARATUN ALKUR’ANI
Babu wata hanyar da za mu gyara
karatun Alku’ani in ba ta hanyar sanin tajwidi ba. Babban abu kuwa shine sanin
mafitar haruffan larabci. Don in har za mu karanta kur’ani da lahajar mu ta
Hausa to, babu shakka za mu dinga caccanza ma’anonin Kur’ani.
Misali, inda Allah Madaukakin Sarki
ke cewa
1.
إنه عليم
بذات الصدور
idan mutum ya karanta da
hamza, أليم
ya canza ma’anar daga Allah masani ne
ya koma Allah mai radadi ne. Subhanallah
2. Haka nan inda Allah (swa) yake cewa مخلصين له الدين
idan mutum ya karanta da sinun مخلسين ya canza ma’anar daga masu yi tsantsa saboda Allah
zuwa masu yankan Aljihu. Subhanallah
3.
Haka
nan inda Allah ke cewa وضل عنهم ما كانو يفترون
Da mutum zai karanta da dalun ودل shi ke nan
mutum ya canza ma’anar daga ya bace musu….
zuwa ya yi musu nuni ……
4.
Har ila yau da mutum zai karanta fadin Allah (swa)
لا تخونوالله والرسول da kafun madadin kha’un
, تكونو لا ma’anar ta canza daga: kada
ku ha’inci Allah da Manzon Allah zuwa kada ku zama Allah da Manzon Allah.
Da sauran irinsu.
Ashe ke nan dole ne mu koyi yadda ake furta kowane harafi na
larabci don mu tsira daga irin wadannan kura-kuran
Aljazari na cewa:
“Dolen dole ne akan (makarantan Alkur’ani )
Ya zama abu na farko tun kafin su fara (karatun alkur’ani) su
san
Mafitar haruffofa da siffofinsu ………
Wanda duk baya karanta kur’ani da tajawidi (ya zama) mai
laifi
Domin da tajwidinsa aka saukar da shi, kuma a hakan ya kawo
zuwa gare mu.”
بســـــــــــــم اللــــــــه الرحمــــــــان
الرحيـــــــــــــم
اللهم رب السماوات السبع و رب العرش العظيم، ربنا
ورب كل شىء فالق الحب والنوى منزل التـــــــــــــوراة والإنجيل و القرآن, أنت الأول
فليس فبلك شـــــــــيء و أنت الآخر فليس بعدك شيء، و أنت الظاهر فليس فوقك شيء و
أنت الباطن فليس دونك شيء
اللهم صل على محمد و على أهل بيته، وعلى أزواجه
وذرياته، كما صليت على آل إبراهيم، إنك حميد مجيد، و بارك على محمد وعلى آل بيته،
وعلى أزواجـــــــه و ذرياته، كماباركت على آل إبراهيم، إنك حميد مجيد
اللهم ربنا تقبل منا ختم القرآن و تجاوز عنا ما كـــان
فى تلاوته من السهو والنسيان واكتبه منا على التمـام والكمال المهذب من كل الألحان.
اللهم اجعل القــرآن لنا فى الدنيا قرينا، وفى القبر مؤنسا، وفى القيامـــــة
شفيعا، وعلى الصراط نورا، و إلى الجنة رفيقا، ومن النار سترا و حجابا و الى
الخيرات دليلا و إماما يـــا أكرم اللأكرمين. اللهم علمنا منه ما جهلنا وذكرنا منه
ما نسينا واروقنا تلاوته وحفظه تأويله آناء الليــــــــل وأطراف النهار على الوجه
الذى يرضيك عنا يا رب العالمين. اللهم اجعلنا من الذين إذا تليت عليهم ءاياتك
زادتهم إيمانا. اللهم اغفر لإخوانن الذين سبقونا بالإيمان, وخصوصاإخواننا حفظ
القرآن الذين قتلوا فى ميدغرى ظلما
اللهم يا خير الراحمين ارحمنا، ويا خير الغافريـــــــن
اغفر لنا، ويا خير الرازقين ارزقنا و يا خير الفاتحين افتح لنا أبواب رحمتك كلها و
خير الناصريـــــــــــن انصرنا، ويا خير حافظ احفظنا بما تحفظ به عبــادك
الصالحين
اللهم بدل عسرنا يسرا، وضيقناسعة, وفقرنا عنـــى,
وضعفنا قوة, وخوفنا أمنا وسلاما واستقرارا لنـــــــا ولسائر المسلمين يا رب
العالمين
اللهم إنا نسألك خشيتك فى الغيب و الشهادة و نسألك
كلمة الحق فى الغضب والرضى،ونسألك القصد فى الفقر و الغنى، ونسألك نعيما لا ينفد و
قرة عيـــن لا تنقطع, ونسألك الرضا بعد القضاء وبرد العيش بعد الموت ومرافقة نبيك
محمد صلى الله عليه وآله وسلم
ولذة النظر إلى وجهك والشوق إلى لقائك فى غيــــر
ضراء مضر ولا فتنة مضلة
اللهم إنا نسألك بأنا نشهد أن لا إله إلا أنت الأحــــــد
الصمد الذى لم يلد و لم يولد ولم يكن له كفوا أحـــد, يــــا ذالجلال والإكرام يا
حي يا قيوم أن تفتح لأدعيتنا أبواب الإجابة يا من إذا سأله المضطر أجابه يامــــــن
فلق البحر لموسى يا فالق الحب والنوى يا حي يا قيوم يــــا ذالجلال والإكرام. ربنا
آتنا فى الدنيا حسنة و فى الآخرة حسنة و قنا عذاب النار
اللهم صل على محمد و على أهل بيته، وعلى أزواجه
وذرياته، كما صليت على آل إبراهيم، إنك حميد مجيد، و بارك على محمد وعلى آل بيته،
وعلى أزواجـــــــه وذرياته، كماباركت على آل إبراهيم، إنك حميد مجيــد
No comments:
Post a Comment