Friday, January 2, 2015

ME YA KAWO HAKA?



ME YA KAWO HAKA??!!
Na dade ina ta tambayar kaina wasu tambayoyi a zuci, har sai da ya kai ga cewa zancen zucina ya fito fili. Amma har yanzu da alkalamina ke rubuta wannan zancen zucin nawa, ban gano amsar da zan ba kaina ba.
Ku taimake ni don mu gano amsar tare.

Tambayar farko:
A zamanin da, malaman addini kan yi amfani da minti biyar kacal, wajen yin wa’azi ga mutane, wa’azin ya ratsa jikinsu, ka ga mutane na kuka suna qauracewa savon Allah ta sanadiyyar wannan wa’azin. Amma me ya sa a yau nake kwashe awa biyar ina wa’azi mai cike da balaga da hikima da qwarewa ta ilimi, amma wa’azin bai ratsa zuciyar mutane balle su bar abinda suke yi na savon Allah???!!! Ka ga idanuwanmu qarmadagau???!!!  

Tambaya ta biyu:
A da, kakata ta haqura ta zauna a gidan mijinta cikin wadatar zuci, ta gamsu da duk abinda kakana zai kawo mata. Amma me ya sa matata a yau ta lashi takobin sai ta fita ta yi aiki, da sunan wai ba komi zan iya yi mata ba, alhali ba na gaza ba ne???!!!

Tambaya ta uku:
Magabatanmu mutane ne masu mutunci da izza. Su ke faxa aji, su ke gitta kara ba’a tsallaka musu, sune iyayen gidan wasu, ba’a yi musu kallon raini. To me ya sa a yau raini da wulakanci ya baibaye mu, ya lulluve mu???!!! A cikin masu raina mun ma har da bayin kakanninmu!!!

Tambaya ta huxu:
A da za ka ga duk inda musulmi ya gamu da xanuwansa musulmi yana xaukarsa tamkar xan gidansu ne uwa xaya uba xaya. Ina irin wannan ‘yanuwantakar ina take a yau???!!!

Tambaya ta biyar:
A da Malamai da almajirai kowa na fafutukar neman lahira ne kawai, ba su siyar da addininsu don samun abin duniya qasqantacce, amma me ya sa a yau ni da malamaina ba mu da aikin yi sai ci da addini???!!!

Tambaya ta shida:
A da idan Musulmi xaya ya shiga wata damuwa gaba xaya za ka ga ‘yanuwansa musulmai sun shiga wannan damuwar; idan kuwa ya faxa hannun arna ne to ko za su qare sai sun je sun ceto wannan xanuwa musulmin. Amma me ya sa a yau mu ke komawa gefe idan wani ko wasu ‘yanuwa suka faxa cikin musiba???!!! Sai abin ya wuce mu kai mu su tsummokara da garin rogo!!!

Wallahi ba wani abu da zai gyara mu in ba abin da ya gyara mutanen farko ba.
Ba wata hanya da za mu bi martabarmu ta dawo in ba mun koma mun kama koyarwar addininmu ba sau da qafa.



No comments:

Post a Comment