Zancen Gaskiya
﴿ظهرالﻔسﺎد فى البر والبحر بما كسبت أيدى
الناس ليذيقهم بعض الذى عملوا﴾
A
lokacin da zan rubuta wannan takarda, babu shakka alqalamina da idanuwana
na kukan baqin cikin yadda a yau
musulmai suka tsinci kansu musamman a Najeriya da kuma duniya baki xaya.
Na
san cewa wannan takardar za ta sha tsokaci, gyara, qarin bayani, sharhi har ma
da raddi. Ina roqon ‘yan uwana ma su yin raddi da su yi raddinsu a bisa adalci
da tsoron Allah.
Mun
ximauce muna neman mafita daga halin da muka tsinci kanmu a yau. Amma duk wanda
ka zauna kana hira da shi sai ka ji yana cewa ai shekarar 2015 ba za mu yarda
ba sai mun kayar da Mai-Nasara na yankin inyamirai. Tunaninmu gaba xaya ya
taqaitu ga samun shugaban da za’a daina kashe mu, mu samu kudi da kwanciyar
hankali. Ba ma tunanin ya ya zamu dawo da martabar addinin Musulunci a qasar;
mu dai a daina kashe mu, mu ci gaba da kasuwancinmu da tara dukiya da mata.
Ina
rantsuwa da sunan Allah, duk wani uzuri da za mu yi ta ba kanmu, da duk wata
hila da kwana-kwana ba za su fitar da mu ba sai mun koma ga addinin Allah, ya
zama Shari’ar Allah ita ke motsi a qasar. Allah Ya sa a fahimce ni a bayanai na
da za su zo a gaba.
Bari
mu kalli qasar gaba xaya ta fuskar:
a) Shugabanci
Haqiqa
duk mai hankali ya san cewa babu wani tsarin mulki babba da ake bi a duniya na
dimokaraxiya ko mulkin soja wanda ba’a yi ba a wannan qasar tamu Najeriya, amma
babu wani sakamako mai kyau da suka haifar in ba kashe shugabanin kirki ba,
ruguza qasa da son maida ita kan wani tafarkin da bai dace da mu ba. Tsarin
mulki xaya ya rage wanda ba’a yi ba a Najeriya, kuma ina rantsuwa da sunan
Allah shine tsarin mulkin da zai kawo dukkan jin daxi da adalci da zaman lafiya
mai xorewa a wannan qasar. Wannan tsarin shine Mulkin shari’ar musulunci. Sai
dai abin tambaya a nan shine shin da irin wannan demokaraxiyar za’a samar da
mulkin musulunci a Najeriya??!!
Wallahi
a tarihin duniya ba’a tava yin haka ba. Ai ya ishe mu kyakkyawan misali abinda
ya faru a qasar Misra (Egypt). Idan can Egypt ya yi mana nisa, to mu tambayi
kanmu da kanmu: Ina makomar shari’ar Zamfara da sauran jihohin arewa?!
A
kullum kira ake ta yi cewa a je ayi rajista, a jefa quri’a, mu zavi mutanen
kirki masu kishin qasa, ba don komi ba sai don a samu zaman lafiya, walwala da
qaruwar arziki. Wani lokaci har mu kan ce “Ai in ba zaman lafiya a qasa ko
addinin ma ba za’a yi yadda ya dace ba.” A dai-dai lokacin mun manta da faxin
Allah cewa:
﴿...
وَالْفِتْنَةُ أَشَدُّمِنَ الْقَتْلِ﴾
ma’ana:
“Yin kafirci (a bayan qasa) shi ya fi yaqi tsanani”
Ai
dai ga shi nan! Kullum siyasar muke yi, zaven mu ke yi, amma kullum cikin
wahala mu ke qara shiga. Daga qarshe, kowa ya ga inda demokaraxiya ta kai mu a
yau. Abin mamaki, waxanda mu ka zava
sune jagororin qasar, amma kuma ga musibu sun baibayemu. Anya! Ba wani abu
kuwa??!! Anya! Ba’a kauce hanyar ba??!! Idan mun ce ma za mu yi demokaraxiyar a
bisa lalura, to me ya sa ba za mu xauki shawarar da babban malami Muhammad
Auwal Adam Albani ya ba musulmin Najeriya ba? [1]
A
wajen duk wani musulmi mai kwana da tunanin addinin musulunci a ransa ya san
cewa hanya xaya ce za ta kai mu ga tabbatar da addininmu a wannan qasar, sai
dai a kullum gudunta mu ke yi, muna cewa wai ba mu
da qarfi, lokaci bai yi ba, sai dai kurin cewa ai muna da yawa a qasar. Hanyar
kawai ita ce JIHADI. Wai! Tabxijan! a nan na san da yawan musulmai za su ce: kun
ji wani mahaukaci, me muke da shi da za mu yi jihadi? Ina rantsuwa da sunan
Allah, wannan xabi’ar ta sa muka manta da cewa jihadi wanzajje ne har zuwa
tashin qiyama. Na cika da mamaki, ranar 17/8/2014 mu na karatu a makarantar
islamiyya babin janaza. Da aka yi maganar yadda ake rufe shahidai, sai wata
mata ta ce “wannan karatun mutanen da ne don yanzu ba jihadi.”[2]
Ka ga har an manta da cewa Annabi (s) ya ce:
مَنْ مَاتَ وَلـَمْ يَغْزُ وَلـَمْ يـُحَدِّثْ
نَفْسَهُ بِهِ مَاتَ عَلَى شُعْبَةٍ مِنْ نِفَاقٍ. رواه مسلم
Ma’ana:
Wanda duk ya mutu bai yi jihadi ba,
kuma
bai ma sa a ransa cewa zai yi jihadi ba, to,
ya mutu a wani bangare
na munafunci.
Jama’a
da gaske na ke yi ina nufin jihadi na gaskiya, ba “jihad week” ba wanda
ake barinsa a “campus” in an gama makarantar, ba jihadin baki ba. waxannan
suna daga cikin abubuwan da suka jawo mana halin da muke ciki. Eh mana! Mun yi
ta kurarin jihadi da baki kawai a qasar nan, wanda hakan ya tsorata wasu mutane
a qasar, su ka shiga tara makamai, daga qarshe da suka gano abin duk bula ne,
sai suka afka mana da kisa da walaqanci a wasu garuruwan arewacin Najeriya.
Allah Ka nuna mana ranar da za mu samu shugaba tsayayye
wanda duk mutanen Najeirya za su yi masa mubaya’a ta yadda in ya yi umurni da
mu fito, shi ke nan an gama. Allah Ka amsa mana. Amin!
A yau gaba xaya mutanen Najeriya sun makauce suna neman
canjin gwamnati. Amma ba gwamnatin addini ba; su dai kawai a samu jin daxi da
walwala. A maimakon musulmi su yi tunanin ya ya za’a ce musulunci ya mulki
Najeriya, sai suma kawai suka koma suka kama tafarkin kafirar siyasar Najeriya,
kai da qafa.
Mu tuna in mun manta cewa tunda Najeriya ta samu ‘yancin kai
har zuwa yau, kafirci ke mulkin Najeriya kuma shi ke jan ragamarsa yadda ya so
a qasar. Me yasa na ce haka? Ta yiwu wani ya ce ia musulmi sun sha yin
shugabanci a Najeriya. Tabbas haka ne, amma ai ba da shari’ar Allah suka yi
shugabancin ba. Kuma ba a lokacin mulkin xaya daga cikin musulman ba ne aka so
a sa qasar cikin qungiyar qasashen musulmi na duniya ba? Amma da qungiyar arnan
Najeriya ta ce ba ta yarda ba, haka nan aka kashe maganar har hazal yaum. Dubi yadda arnan arewa suka afka ma musulmi a garuruwan
Jos da Yalwan Shandam …. a nan arewacin Najeriya, suka kashe mutanenmu, suka
qona dukiyoyinmu, suka kwashe matayenmu waxanda har yau suna can a hannunsu
amma ba abinda aka yi. Gwamnati ba ta yi komai ba, mu kuma son duniya da tsoron
mutuwa sun hana mu yin wani abu; kamar yadda Annabi (saw) ya faxa. Dubi irin
kisar da suka yi ma musulmi a ranar sallah. Wai ina ‘yanuwantakar musulunci da
ke tsakaninmu, wanda abin nan ya afku, ba xaya ba ba biyu ba, amma ba wani
xauki da musulman qasar nan suka kai. Sai da aka gama abinda aka yi mu ka tara
tsummokara da garin rogo mu kai musu. Abinda muka iya ke nan. A yau kuwa Mai-Nasara na yankin inyamirai da
qungiyar arnan Najeriya sun haxa kai sai sun ga bayanmu. Ba su son su ga muna
addininmu. A nan na ke son ‘yan-uwa musulmi su san cewa samu daular duniya a
qarqashin rashin bin dokar Allah, wahala ne kawai. Allah Ya kai haske qabarin Alfazazi
da ya ce:
إِﺫَاالدِّينُ لَمْ يَكْمُلْ فَلاَ كَانَتِ
الدُّنْيَا
Idan har
ba za’a yi addinin (Allah)
ba (a bayan qasa) to, babu amfanin wanzuwar duniya (gwamma duniyar
ta tashi)
Ya ku ‘yan uwana musulmin Najeriya, muna tunanin a yau
idan aka buga kugen siyasa, muka zavi xan arewa musulmi, shi ke nan arnan nan
za su bar mu a irin qarfi da xaurin gindin da suke da shi a qasar da sauran
qasahen duniya masu goyon bayan ta’addanci?! Qarfinsu a yau ya kai ga su yi
odar makamai jirgi guda wanda gwamnatin tarayya ce kawai zata iya sayen irinsu,
kuma huxxar cinikinsu ma sai qasa da qasa.
Sai dai qungiyar CAN ba ta yi laifi ba. Eh, mana! Mu fa
Allah Ya gaya mana a cikin qur’aninmu cewa:
﴿
وَأَعِدُّوا لـَهُم مَّاسْتَطَعْتُم مِّن قُوَّةٍ وَ مِن رِبَاطِ الـْخَيْلِ تُرْهِبُونَ
بِهِ عَدُوَّ اللهِ وَعَدُوَّكُمْ ﴾
Ma’ana: Ku yi musu tattali na qarfi (makaman harbi) da turkakun dawakai don razanar da
maqiyan Allah kuma maqiyanku
Amma abin mamaki gaba xaya musulman
Najeriya mun yi shakulatin vangaro da wannan umurnin na Allah.
Su
kuwa da Bible ya ce musu a cikin Luke 22: 36 “ …And he who has no sword, let
him sell his garment and buy one.” Ma’ana: “…. Duk wanda ba shi da makami
to, ya sayar da suturarsa ya sayi (makami).” Sai ga shi har odar jirgin makamai su ke yi. Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un
b)
Zamantakewa da rayuwa
A
sanadiyar rashin gwamnatin musulunci mai adalci, a yau mutanen Najeriya na
rayuwa ne yadda suka ga dama. Har ta kai ga cewa idan mutumin kirki ya aikata
wani aikin da addinin musulunci ya yi umurni da shi, sai ka ji ana cewa ai su malam wane akwai
takura ma kai. Dubi yadda zina, shan giya, luwaxi, maxigo su ka bayyana a qasar
nan. Cin haramun da riba kuwa waxannan ‘yan gida ne. Abin takaici shine yadda
matan aure suka nutsa cikin harkar zina. Aiki ba da ilimi ba kuwa ya zama ado a
gunmu. Zumunta sai wane da wane. Son juna kuwa a baki ne kawai. ‘Yan uwantakar
musulunci sai kaxan. Kar ma mutum ya yi maganar haxin kai don babu. Taimakon
addini a wajenmu shine kawai mu gina masallatai, Don haka a yau muka cika
anguwanninmu da garuruwanmu da masallatai waxanda kawai muke cika su jikinmu.
Kamar dai yadda Annabi (saw) ya ce: “……sun
cika masallatansu da jikinsu amma zuciyarsu ta rushe daga shiriya.” Dukkan waxannan halayen, rashin tsayayyar
gwamnatin musulunci ya sa suka zama ruwan dare a qasarmu. Mafi munin al’amarin
shine ba mu da wani jagora ma takamaimai mai faxa aji.
Ya
ku musulman Najeriya babu shakka an fa ci mu da yaqi, duk wani abu da za’a yi
mana a yau mai-mai ne. Jama’a an fa tsere mana, duk wani sauri ko gudu da za mu yi don mu cimma
waxancan, tafiyar guragu ce kawai.[3]
TO YANZU INA MAFITA?
Mafitar ita ce
1)
Fadin Allah Maxaukaki da yake cewa
﴿وَعَدَ
اللهُ الَّذِينَ ءَامَنُوا مِنْكُم وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ لَيَسْتَخْلِفَنَّهُمْ
فِى الْأَرْضِ كَمَا اسْتَخْلَفَ الَّذِينَ مِن قَبْلِكُمْ وَلَيُمَكِّنَنَّ لَهُم
دِينَهُمُ الَّذِى ارْتَضَى لَهُمْ وَلَيُبَدِّلَنَّهُمْ مِنْ بَعْدِ خَوْفِهِمْ أَمْنًا
يَعْبُدُونَنِى وَلَا يُشْرِكُونَ بِى شَيْئًا
وَمَنْ كَفَرَ بَعْدَ ذَالِكَ فَأُولَـــئِكَ هُمُ الْفَاسِقُونَ
﴾ سورة
النور : ٥٥
Ma’ana:
Allah
Ya yi alqawari ga waxanda suka yi imani suka aikata aiki na qwarai cewa Zai
sanya su, su zama mamaya a cikin qasa, kamar yadda Ya sanya waxanda suka zo
kafin ku; kuma (Allah) Zai tabbatar musu da addinsu wanda Ya yardar musu a gare
su; kuma Allah Zai canza musu bayan tsoron da suke ciki zuwa zaman lafiya, su
bauta mini batare da suna haxa ni da kowa ba. Duk waxanda suka kafirce bayan
wannan to, waxannan sune fasiqai.
Bari mu dubi
ayar nan da kyau
i.)
Allah Ya yi alqawari ga waxanda suka yi imani suka aikata aiki na
qwarai …..
babu
shakka imani na gaskiya shine matakin farko na cin nasarar duniya da lahira.
Aiki na kwarai kuwa Annabi (saw) ya yi bayaninsa a lokacin da aka tambaye shi
wane aikin alheri ne ya fi kowanne? Sai ya ce: JIHADI DON XAUKAKA KALMAR
ALLAH. (Muslim)
ii.)
(Allah) Zai tabbatar mana da addinmu wanda Ya yardar mana a gare mu; kuma
Zai canza mana tsoron da muke ciki zuwa zaman lafiya.
Alqawarin
Allah da Ya yi mana a wannan ayar Ya yi ne bisa sharaxin in mun yi imani kuma
mun yi aiki na qwarai.
Ashe ke nan
matakin farko shine mu kyautata imaninmu, mu so juna so na haqiqa wanda babu khiyana a ciki. Daga nan sai mu
roqi Allah Ya ba mu jagora tsayayye wanda duk wani musulmi zai yi masa
mubaya’a. wannnan shine ginshiqin da muka rasa don haka muka kasance cikin ruxu
da hayaniya, kowa na abinda ya ke so.
2) Faxin
Annabi (saw) da ya ce:
“Idan dai ku ka koma (ba abinda ku ka sani kuma ba abinda
ku ke yi) sai noma da kiwo, ku ka bar jihadi; Allah Zai xora muku wani irin
walaqancin da ba Zai cire muku shi ba har sai kun koma zuwa ga
addininku (da gaske kamar yadda ya ke.)” Wannnan kuwa ba mai musun cewa
haka muka koma a yau. Maza da mata yaro da babba ba abinda muka tasa a gaba sai
neman duniya. Inna lillahi wa inna ilaihi raji’una! A yau akwai matayen
da ke kashe auren su don su koma makaranta, wai in sun gama su samu aiki a dama
da su.
Allah Ka ba mu zaman lafiya mai xorewa. Ka qare mu da
lafiyar da za ta zamo mana qarfi wajen rusa kafirci da zalunci a wannan qasar
tamu mai albarka.
No comments:
Post a Comment